‘Yan sanda na gudanar da bincike kan kwarmata tambayoyin jarabawar Lissafi ta makarantar gaba da Sakandare tare da cafke mutane biyu da ake zargi.
A ranar Litinin ne ‘yan sandan suka kama mutanen biyu da ake zargi da kwarmata tambayoyin, mace ‘yar shekara 29 da namiji dan shekara 32.
Bayan yi musu tambayoyi ‘yan sanda sun sallame su tare da ci gaba da sanya musu ido yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike.
An dai wallafa tambayoyi biyu na jarabawar lissafi a shafin Twitter, wadda aka rubuta a ranar 14 ga watan Yuni.
Sannan a kasan tambayoyin aka bukaci daliban da suke da sha’awar sanin sauran tambayoyin su biya fan din Ingila 70, kwatankwacin Naira 32,000.
Tuni dai aka goge wannan bayanin daga shafin Twitter.
Shugaban makarantar da aka rubuta jarabawar ya ce ya san burin duk wani dalibi shi ne ya samu sakamakon jarabawa mai kyau, to amma ba ta barauniyar hanya ba.
A dan tsakanin nan batun satar jarabawa da kwarmata tambayoyin jarabawar gabannin yin ta na ci gaba da zama batun da ke ciwa hukumomin kasashen da ke fama da matsalar tuwo a kwarya.
Ko a farkon watannan kasar Habasha sai dai ta toshe internet a wasu sassan kasar da dalibai ke rubuta jarabawa duk domin kaucewa satar amsa.