An damke tsohon minista Adoke a Dubai

Adoke

Hukumar ‘yan sandan kasa da kasa watau Interpol ta damke tsohon ministan shari’ar Najeriya bisa zargi sa da hannu a wata badakalar cin hanci kan danyen mai na fiye da dala biliyan daya.

Lauyan Mr Mohammed Bello Adoke ya tabbatar da tsare tsohon ministan a Dubai, amma ya ce bisa wani sammaci ne da lokacinsa ya wuce.

A baya Mr Adoke ya ce bai ci komai ba game da wata yarjejeniyar sayar da wata rijiyar mai a shekara ta 2011.

A cikin watan Afrilu ne hukumar yaki da rashawa a Najeriya – EFCC ta ba da sammacin kama shi tare da tsohon ministan man kasar, Dan Etete da kuma wani manaja a kamfanin mai na Italiya mai suna Eni.

Lamarin ya janyo shari’a mai tsawo tsakanin gwamnatin Najeriya da wasu kusoshi a kamfanonin mai na Eni da kuma Shell.

Sai dai duk kamfanonin biyu sun musanta aikata ba dai-dai ba.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...