An ceto mutane uku daga wani gini da ya ruguzo a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta ce mutane uku aka ceto daga cikin baraguzan ginin bene da ya ruguzo a yankin Garki dake birnin tarayya Abuja.

Ƴan sanda sun bayyana sunan ginin da ya ruguzo da Unity House dake kan titin Nkwere kuma ya ruguzo ne ranar Litinin da daddare.

A wata sanarwa da aka fitar ranar Talata, Josephine Adeh mai magana da yawun ƴan sandan birnin ta ce, Benneth Igweh kwamishinan ƴan sandan birnin ya jagoranci tawagar jami’an ƴan sanda ya zuwa biyo bayan kiran kai ɗaukin gaggawa da rundunar ta samu.

Mai magana da yawun rundunar ta ce hukumomin da abun ya shafa na cigaba da saka idanu akan lamarin.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]