Ƴansanda sun gurfanar da yan shi’a sama da mutane 100 a gaban wata kotun majistire dake Abuja inda ake zarginsu da ta da hankalin al’umma.
Cikin yan kungiyar ta shi’a sama da 100 da aka gurfanar a gaban kotun a ranar Alhamis, 10 daga cikinsu mata ne.
An kama sune ranar Talata lokacin wata zanga-zanga da ta rikide zuwa tarzoma a yankin Wuse dake Abuja.Sun dade suna zanga-zangar neman a saki shugaban su, Ibrahim Elzakzaky wanda ke hannun jami’an tsaro.
Ƴansanda sun ce cikin abubuwan da aka gano a tare da su har akwai kawalaben bom na fetur.
Dukkannin mutanen sun ki amsa tuhumar da ake musu kana sun nemi a a basu beli.
Kotun majistiren ta bayar da belinsu kan kudi kama daga ₦50000 zuwa ₦200000 da kuma mutanen da za su tsaya musu.
An dage zaman shari’ar ya zuwa ranar 5 ga watan Disamba.