An ba wa sojoji tukwici saboda ƙin karɓar cin hanci daga wasu ɓarayin shanu

Rundunar soji ta musamman mai kula da wanzar da zaman lafiya a jihar Filato ta bayyana cewa, a ranar Talata, ta bayar da tukwici ga wasu jami’an ‘Operation Safe Haven’ guda takwas bisa kin karbar cin hancin N1.5m daga wasu da ake zargin barayin shanu ne a jihar.

Kakakin rundunar, Kaftin Oya James, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Talata, ya ce jami’an 8 da aka tura a sashin OPSH 4, sun kama wasu barayin shanu 30 a shingen binciken Bisichi da ke karamar hukumar Barkin Ladi ta jihar.

A cewarsa, an yi awon gaba da shanun wani Shehu Umar ne a garin Mangu kuma ana ƙoƙarin kai su zuwa wani wuri da ba a bayyana ba.

Har sai da dakarun rundunar da ke aikin kawo lumana suka tare su.

More News

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...

Gwamnati za ta fara biyan ma’aikata naira 30,000 mafi ƙarancin albashi a Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya sanar da cewa za su fara aiwatar da tsarin mafi ƙarancin albashi naira 30,000 ga ma'aikatan jihar...

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...