Amurka ta tura karin dubban sojoji saboda barazanar Iran

US Marine

Hakkin mallakar hoto
AFP

Ma’aikatar tsaro ta Pentagon ta sanar da tura karin dubban sojojin Amurka domin “Kara karfin kariya ga Saudiyya”.

Sakataren Tsaro na Amurkar, Mark Esper ya ce ya amince da aikewa da karin dakaru da suka hada da jiragen yaki da kuma na’u’rorin kariya.

Ya ce hakan martani ne ga “irin barazanar da yankin ke fuskanta”, a dai-dai lokacin da ake rubanya kokarin kare masarautar daga “hare-haren Iran”.

Wannan dai na zuwa ne bayan da aka kai har kan matatun man kasar Saudiyya a watan Satumba.

Yanzu haka dai Amurka ta kara dakaru 14,000 a yankin gabas ta tsakiya tun watan Mayu, kamar yadda gidan talbijin na CNN ya rawaito.

Tun dai lokacin da aka kai wa matatun man Saudiyya harin jirgi maras matuki, al’amarin da ya lalata su, ake ta zargin kasar Iran da hannu.

Tuni dai Iran ta musanta kai harin.

Su ma shugabannin kasashen France da Jamus da Burtaniya sun ce babu wata kwakkwarar sheda cewa Iran din ce ta kai harin.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...