Amurka da Burtaniya sun ce mai yuwuwa kungiyar Taliban da ke yaki a Afghanistan ta aikata laifukan yaki a hare-haren da take kaiwa a kwanan nan.
A sanarwar da suka sanya a shafin tuwita, ofisoshin jakadancin kasashen biyu da ke Kabul, sun yi bayani sosai a kan abin da suka kira kisan kiyashin farar hula a garin Spin Boldak da ke kan iyaka da Pakistan. Sai dai kungiyar Taliban ta yi watsi da zargin.
Kamar yadda wannan yaki yake kara tsananta a fadin Afghanistan, haka ma kuma ake kara nuna damuwa a kan irin keta haddi da cin zarafin da ake yi a fagen dagar.
Yawanci ana mayar da hankali ne a kan zargin keta haddi da saba ka’ida da mayakan Taliban ke yi ne, da suka hada da yadda suke kai wa sojojin gwamnatin Afghanistan da kuma farar hula hare hare.
A kwanan nan aka ga wasu hotunan bidiyo na irin keta haddi da tsabagen rashin Imani ko tausayi da mutunta dan adam, da aka yi a garin kan iyaka na Spin Boldak, abin da ya harzuka jama’a da hukumomi, wanda ya sa a yanzu Amurka da Burtaniya ke neman da a gudanar da bincike na yuwuwar gano laifukan yaki da aka aikata.
A wadannan makonni na karshen ayyukan sojojin hadaka da Amurka ke jagoranta, gwamnatin Amurka na ta gargadin ‘yan Taliban, inda a fili take sukar hare-haren da suke kaiwa yanzu.
To amma kuma a Litinin din nan Shugaba Ashraf Ghani na Afghanistan, yayin jawabinsa a majalisar dokokin kasar, na cike da Amurkar, inda ya dora alhakin kazantar yakin da ake yi yanzu a kan matakin da gwamnatin Shugaba Biden ta dauka na janye dakarunsu.
Shugaban na Afghanistan ya ce, abin da ya jefa su halin da suke ciki yanzu shi ne saboda wata shawara da aka yanke.
Ya fayyace cewa na gaya wa Shugaban Amurka, ina mutunta matakin naka, saboda, ra’ayinka ne, to amma na kwana da sanin yana da illa.
Kalaman Shugaban na Afghanistan sun zo ne yayin da ake ta suka a majalisar dokokin kasar ta Afghanistan, da kuma damuwa da bacin rai da jami’an Amurka da Burtaniya ke nunawa a bayan fage, cewa shirin Shugaba Ghani na soji ya gaza.
Ana ganin sakamakonsa a fili karara inda ‘yan Taliban ke ci gaba da mamaya a fadin kasar ta Afghanistan. Lamarin ya kai har ta kusa kama birni na biyu mafi girma a kasar, Kandahar.
Kuma rayuwar jama’a na cikin halin kaka-ni-kayi, kamar yadda shugaban wata kungiyar bayar da taimakon ilimi, Pashtana Durrani ya gaya wa BBC:
Ya ce: ”Na yi kuka sosai da idona, saboda ba abin da ake yi sai harbe-harbe da ruwan bama-bamai duk tsawon dare, da kuma safiya. Ba abin da kake gani sai harsasai a bayan gidanka da gaban gidanka.
Duk lokacin da ka duba wayarka za ka ga wani a cikin ‘yan uwanka ya mutu, wani a gundumarku ya mutu, wani da ka sani ya mutu, wani da ka sani na gudu daga kasar, wani da ka sani na tserewa daga lardin, wannan kawai kana rayuwa ne cikin tashin hankali.”