Tsohon dan wasan Najeriya, Emmaneul Amuneke ya ce zai fuskanci babban kalubale, bayan da ya karbi aikin horas da El-Makkasa.
El-Makkasa mai buga gasar Premier ta Masar tana cikin ‘yan kasa-kasan teburi, inda Amuneke zai ja ragama zuwa karshen kakar bana.
Amuneke, mai shekara 49, zai maye gurbin Ahmed Hossam Mido ranar Asabar, kuma zai zama mai horas wa na hudu da kungiyar ta dauka a shekara uku.
Wannan karon Amuneke zai koma Arewacin nahiyar Afirka da sana’ar horas da tamaula, bayan da a baya can ya taka leda a yankin.
Tsohon dan kwallon Barcelona da Sporting Lisborn, ya koma Zamalek daga Julius Berger ta Lagos a 1991.
Amuneke ya ja ragamar tawagar Tanzaniya a karon farko tun bayan 1980 da kasar ta kai gasar cin kofin nahiyar Afirka.
Sai dai kasar ba ta taka rawar gani ba, inda aka yi waje da ita a wasannin cikin rukuni, hakan ne ya sa Amuneke da hukumar kwallon kafar Tanzaniya suka raba gari cikin fahimtar juna.
Amuneke ya horar da matasan tawagar kwallon kafa ta Najeriya da kuma kungiyar Sudan mai suna SC Khartoum.