Afirka ta Kudu ta nemi gafarar Najeirya a kan hare-haren kin jinin bakin da aka kai wa ‘yan Najeriya da ke kasar.
Jakada na musamman na gwamnatin Afirka ta Kudu, Jeff Radebe, ya gabatar da takardar neman afuwar a madadin Shugaba Cyril Ramaphosa, a wata ganawa da yi da Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a fadarsa da ke Abuja.
Da alamu gwamnatin Afirka ta Kudu na kokarin kyautata alakarta da sauran kasashen Afirkan wadanda hare-haren kin jinin baki a Afrika ta Kudun ya shafa.
Jami’in na Afirka ta Kudu, ya shaida wa shugaba Buhari a Abuja cewa gwamnatin Afirka ta Kudu ta yi Allah-wadai da tashe-tashen hankulan da aka samu, kuma ya ce tana daukar kwararan matakai.
A yayin da Afirka ta Kudu ta dauki wannan mataki, Najeriya na ci gaba da kwashe ‘yan kasarta daga Afirka ta Kudu.
Ana sa ran isowar wani rukuni na ‘yan Najeriya 319 daga Afirka ta Kudu a filin jirgin sama da ke Legas a ranar Talata.
Sai dai Shugaba Buhari ya tabbatar wa jami’in cewa za a kara kyautata dangantaka tsakanin kasashen biyu.