Adadin Masu Coronavirus a Najeriya Ya Doshi 5000 | VOA Hausa

Sabbin alkaluman da hukumar dakile yaduwar cututtuka a Najeriya ta NCDC ta fitar, sun yi nuni da cewa mutum 146 sun sake kamuwa da cutar cikin yinin jiya Talata.

Har yanzu dai Legas ce ke kan gaba wajen samun yawan masu dauke da cutar, inda yanzu ta sake samun sabin mutum 57.

Baya ga Legas, jihar Kano wacce ta ke fama da yawan mace-mace a ‘yan kwanakin nan ita ma ta samu mutum 27 da suka kamu da cutar.

Ya zuwa yanzu adadin masu cutar ya kai 4,787 a duk fadin kasar.

Adadin masu rasuwa sakamakon cutar shi ma yana dada haurawa, inda a cikin yinin jiya kawai aka samu mutum 8 da suka mutu sakamakon cutar.

Hakan ya mayar da adadin wadanda coronavirus ta kashe zuwa 158.

Masu samun waraka su ma sun kara yawa, inda yanzu Najeriya ke da mutum 959 da suka warke daga cutar.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

ÆŠan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...