Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ya sake yin bulaguro zuwa birnin London bayan kammala taron kasuwanci na duniya na yini uku a birnin Riyadh na Saudiyya.
A ranar Asabar ne Shugaba Buhari ya bar kasar Saudiyya zuwa Birtaniya, daga nan ya dawo Najeriya.
Fadar shugaban ta ce ya tafi London ne bisa radin kansa, ba tare da cikakken bayani ba, duk da ce-ce-ku-ce kan yawan tafiye-tafiyensa.
Shugaban ya ziyarci kasashen Japan da Rasha da Afirka ta kudu da kuma Amurka kafin ya tafi zuwa Saudiyya.
Babbar Jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta ce ‘babu wata riba da kasar ta samu’ daga yawan tafiye-tafiyensa zuwa kasashen waje.
Sai dai fadar shugaban ta ce kimar shugaban da darajarsa a idon kasashen duniya ne ya sa ake yawan halartarsa taro kuma tafiye-tafiyensa suna da muhimmaci ga ci gaban kasar.
Ana sa ran Shugaba na Najeriya zai dawo Abuja a ranar 17 ga watan Nuwambar 2019.
Idan har Buhari ya koma zai kasance kwanaki 425 ke nan shugaban ya yi a kasashen waje a tsawon shekara hudu da rabi na mulkinsa.