Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci hukumar zaben kasa INEC ta tabbatar da yin adalci a zabukan cike gurbi da za a yi a watan Janairu da kuma na nan gaba.
Shugaban ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da shugaban hukumar zaben kasar Mahmoud Yakubu da Supeton ‘yan sanda Muhammad Adamu, wadanda suka je domin yi masa karin bayani dangane da yadda zabukan 2019 suka kasance da kuma shirin da aka yi na karasa wasu da ba a kammala ba a watan Janairu.
A sanarwar da mai taimakawa shugaban kasar ta fuskar yada labarai Femi Adesina ya fitar, shugaba Buhari ya bukaci INEC ta tsaya kaida fata wajen yin adalci da kuma bin doka a dukkanin zabukan da zata gudanar, ta yadda ‘yan Najeriya da ma duniya baki daya zasu yi amanna da ingancin zabukan.
“Dole ne kowanne dan Najeriya ya samu damar zabar duk wanda yake so ba tare da fuskantar wani kalubale ba” Inji shugaba Muhammadu Buhari.
Wannan dai na zuwa ne bayan kammala zabukan jihohin Kogi da Bayelsa, da kungiyoyin masu sanya ido na ciki da wajen kasar suka ce an tafka magudi da keta doka a cikin sa.
‘Yan adawa sun ce ba abin da zai sauya a zabukan cike gibin da za a gudanar.
Injiniya Buba Galadima daya daga cikin manyan masu hamayya da gwamnatin APC ya ce “shugaban ya sha fadar za a yi zaben adalci amma abin da ya faru a Kogi da Bayelsa ya nuna ba abin da zai sauya.”
Sai dai a nata bangaren hukumar zaben kasar ta ce tana bakin kokarinta wajen tabbatar da ganin ana samun ci gaba a zabukan kasar.