AA Zaura ya kalubalanci nasarar Rufa’i Hanga a gaban kotu

Ɗantakar jam’iyyar APC a zaɓen sanatan Kano ta tsakiya, Alhaji Abdulsalam Abdulkarim Zaura ya shigar da ƙara a kotun sauraron kararrakin zabe dake Kano inda yake kalubalantar nasarar da Rufa’i Sani Hanga ya samu na jam’iyyar NNPP.

Zaura ta hannun lauyansa, Ishaka Dikko ya roki kotun da ta ayyana shi a matsayin wanda ya lashen zaɓen kana ta jingine sanarwar da hukumar zaɓe ta INEC ta yi da baiwa Hanga nasara.

Ya yi zargin cewa zaɓen sanatan Kano ta tsakiya na cike da kura-kurai da kuma saɓa ka’idar dokokin zaɓe.

Amma kuma a martaninsu hukumar zabe ta INEC, Hanga da jam’iyar NNPP sun dage cewa an yi zaɓen kamar yadda dokar zabe ta shimfida.

More News

An Jikkata Jami’an Tsaro A Harin Da Ƴan Bindiga Su ka Kai Wa Ayarin Motocin Yahaya Bello

A jikkata wasu jami'an tsaro a wani hari da yan bindiga su ka kai kan jerin ayarin motocin gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ranar...

Bala Muhammad ya zama shugaban gwamnonin jam’iyyar PDP

An zaɓi gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad a matsayin sabon shugaban kungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP. Siminalayi Fabura zaɓaɓɓen gwamnan jihar Rivers shi ne mataimakin shugaban...

Za mu sake bitar mafi karancin albashi a Najeriya—Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya yi alkawarin sake nazarin mafi karancin albashin ma’aikata domin dacewa da yanayin tattalin arzikin kasar nan. A cewarsa, akwai bukatar...

EFCC na zargin tsohuwar ministar mata a mulkin Buhari da karkatar da naira biliyan 2

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati ta titsiye tsohuwar ministar harkokin mata Pauline Tallen kan zargin azurta kai ta...