A lura sosai game da yadda jabun takardun naira suka yawaita—CBN ya gargadi ƴan Najeriya

Babban bankin Najeriya, CBN, ya gargadi ‘yan Najeriya da su yi hattara da kudaden Naira na bogi da ke yawo ba bisa ka’ida ba.

Wannan gargadi na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mukaddashin daraktan sadarwa na CBN, Hakama Sidi Ali, ta fitar a Abuja ranar Juma’a.

“An jawo hankalin Babban Bankin na CBN a kan yadda ake yada takardun kudi na jabu, musamman manyan kuɗaɗen da wasu mutane ke yi,” in ji ta.

Sidi Ali ya te jabun na Naira an fi amfani da shi wajen hada-hadar kasuwanci a kasuwannin abinci da sauran cibiyoyin kasuwanci a fadin manyan kasuwanni a garuruwan kasar.

Ta ce duk wanda aka samu da hannu wajen shigar da kudaden na jabu to zai fuskanci hukunci mai tsanani.

Draktar ta ce dokar ta tanadi hukuncin zaman gidan yari wanda ba zai yi kasa da shekaru biyar ba, ga duk wanda aka samu da laifin yin jabun kudin Naira ko kuma duk wata takardar doka a Najeriya.

“CBN na ci gaba da hadin gwiwa da hukumomin tsaro da wadanda suka dace domin kwato takardun kudin Naira na bogi, kamawa da hukunta masu yin jabun.”

“Ana kuma kara kira ga jama’a da su kai rahoton duk wanda ake zargin yana da kudin jabun naira ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa, reshen CBN, ko ta contactcbn@cbn.gov.ng,” in ji ta.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...