Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmed Nuhu Bamalli, ya yi kira ga jami’o’in Najeriya da su inganta tsarin ilimi tare da rungumar sabbin fasahohi, musamman basirar wucin gadi (AI).
Sarkin ya bayyana cewa haɗa ilimin gargajiya da sabbin fasahohi zai bai wa ɗalibai ƙwarewar da za ta taimaka musu wajen gogayya a tattalin arzikin duniya.
Ya yi wannan magana ne a wani taron ƙasa da ƙasa da Tsangayar Ilimin Kimiyyar Zamantakewa ta Jami’ar Ilimi ta Tarayya da ke Zariya ta shirya.
Sarkin ya ce ilimi shi ne ginshiƙin ci gaban ƙasa, don haka jami’o’i ya kamata su kasance kan gaba wajen samar da sabbin hanyoyin magance matsalolin da al’umma ke fuskanta.
Ya kuma buƙaci masu bincike da masu tsara manufofi su ƙara mayar da hankali kan binciken da zai samar da mafita ta cikin gida, tare da amfani da ƙirƙire-ƙirƙire da haɗin gwiwa.
Sarkin Zazzau Ya Bukaci Jami’o’i Su Rungumi Fasahar AI

