‘Yan Sanda Sun Kama Budurwa Da Ake Zargi Da Yanke Mazakutar Saurayinta A Kano



Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta kama wata matashiya mai shekaru 25 da ake zargi da yanke mazakutar saurayinta yayin da yake barci a wani otal da ke unguwar Badawa a birnin Kano.

Kakakin rundunar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce dukkansu ‘yan Jihar Jigawa ne da suka sauka a otal ɗin. Ya bayyana cewa wannan ne karon farko da rundunar ta samu irin wannan lamari da aka yanke mazakutar namiji gaba ɗaya.

A cewarsa, wadda ake zargin ta shaida wa ‘yan sanda cewa ta aikata hakan ne lokacin da saurayin yake barci. Bayan haka, ta ja shi zuwa banɗaki domin wanke jinin da ya zuba kafin jama’a su fahimci abin da ya faru.

Kiyawa ya kuma ce ana bincike kan wasu abubuwan sha da jami’ai suka samu a ɗakin, domin gano ko suna da alaƙa da lamarin. Ya ƙara da cewa, bisa bayanan farko da aka tattara, babu wata shaida da ke nuna cewa saurayin ya sha kayan maye kafin faruwar lamarin.

More from this stream

Recomended