Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa akalla ‘yan kasarta 98 sun mutu a hare-haren ƙyamar baƙi a Afirka ta Kudu tun daga 2022, yayin da kusan mutum 1,500 suka tsere daga ƙasar bayan an lalata gidajensu da dukiyoyinsu.
Ƙaramin Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Sola Enikanolaiye, ya zargi gwamnatin Afirka ta Kudu da gaza kare ‘yan Najeriya da sauran baƙi da ke zaune a ƙasar bisa ka’ida.
Sai dai gwamnatin Afirka ta Kudu ta musanta cewa tana goyon bayan ƙyamar baƙi. Ministan Hulɗar Ƙasa da Ƙasa, Ronald Lamola, ya ce an kama wasu da ake zargi da kai hare-haren, kuma za a gurfanar da su a kotu.
Kasashen biyu sun kuma amince da ci gaba da tattaunawa kan batutuwan tsaro da hijira domin ƙarfafa dangantakarsu da kuma kare rayukan baƙi.
Najeriya Ta Ce ‘Yan Kasarta 98 Sun Mutu A Hare-Haren Ƙyamar Baƙi A Afirka Ta Kudu

