Tinubu ya rantsar da sababbin ministoci biyu

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu a ranar Litinin ya rantsar da Joseph Tegbe a matsayin sabon ministan wutar lantarki da kuma Ambasada Sola Enikanolaiye a matsayin ƙaramin ministan ma’aikatar harkokin waje.

An gudanar da bikin rantsuwar ne fadar shugaban ƙasa dake Abuja inda ta asamu halartar iyalan mutanen da kuma manyan jami’an gwamnati.

An naɗa mutanen biyu mukamin ministoci ne  biyo bayan murabus ɗin da ministan harkokin waje, Yusuf Maitama Tuggar ya yi domin ya tsaya takarar gwamna a jihar Bauchi a yayin da takwaransa na wutar lantarki Bayo Adelabu ya tsaya takarar gwamna a jihar Oyo.

Bayan murabus din nasu ne Tinubu ya zaɓi Tegbe da Enikanolaiye a matsayin wanda za su maye gurbinsu kuma majalisar datttawan Najeriya ta tabbatar da su a matsayin ministoci a ranar 6 ga watan Mayu.

Tegbe ɗan asalin garin Ibadan ne ta jihar Oyo a  yayin da Enikanolaiye ya fito daga jihar Kogi.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]