Tinubu Ya Sha Alwashin Najeriya Ba Za Ta Mika Wuya Ga ‘Yan Ta’adda Da ‘Yan Bindiga Ba



Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ba za ta taɓa mika wuya ga ta’addanci, ƴan bindiga ko duk wata barazana daga masu aikata laifuka ba.

Sakon shugaban ya fito ne ta bakin Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, a wani taron addu’ar Kiristoci da aka gudanar a Abuja domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya ta shekarar dubu biyu da ashirin da shida.

Tinubu ya ce gwamnati na sane da matsalolin tsaro, garkuwa da mutane da kuma wahalhalun tattalin arziki da al’umma ke fuskanta, yana mai tabbatar da cewa ana ɗaukar matakan da suka dace domin magance su.

Ya kuma bayyana cewa dawo da mutanen da ke hannun masu garkuwa da su cikin koshin lafiya na daga cikin manyan abubuwan da gwamnati ta sa a gaba.

A cewarsa, jami’an tsaro na samun goyon bayan kayan aiki da sauran abubuwan da suke buƙata domin kare rayuka da dukiyoyi tare da tabbatar da tsaron ƙasar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]