Ƴan Sanda Sun Kama Matar Da Ta Yada Rahoton Karya Kan Sace Dalibai a Edo

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Edo ta kama wata mata mai suna Uzebor Emmanuel, wadda aka fi sani da “Aza Woman”, bisa zargin yada rahoton karya cewa an yi garkuwa da wasu dalibai a makarantu biyu da ke Benin City.

Rahotanni sun nuna cewa matar ta wallafa wani bidiyo a kafafen sada zumunta inda ta yi ikirarin cewa wasu ‘yan bindiga sun kutsa makarantu tare da sace dalibai shida. Ta kuma ce wasu daga cikin daliban sun tsere yayin da wasu suka biya kudin fansa.

Sai dai kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Eno Ikoedem, ya ce bincike ya nuna cewa bayanan ba gaskiya ba ne. Ya bayyana cewa rahoton ya haddasa fargaba a tsakanin jama’a tare da iya raunana amincewar al’umma ga tsarin tsaro na jihar.

Rundunar ta ce za a gurfanar da wadda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike. Haka kuma ta bukaci jama’a su rika tantance sahihancin bayanai daga amintattun hanyoyi kafin yada su a kafafen sada zumunta.

More from this stream

Recomended