Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa Isra’ila ba za ta kasance a halin yanzu ba da ba don irin matakan da ya dauka ba, yayin da ya yi watsi da zarge-zargen cewa Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ne ya rinjaye shi wajen shiga takun-saka da Iran.
Trump ya yi wannan bayani ne a wata hira da aka yi da shi a shirin Pod Force One, inda aka tambaye shi kan ikirarin cewa Netanyahu ne ya jawo shi cikin rikicin da ke tsakanin kasashen biyu.
Ya bayyana cewa matakinsa ya samo asali ne daga damuwa kan shirin nukiliyar Iran.
Kalaman shugaban na Amurka sun zo ne a lokacin da ake samun rahotannin sabani tsakaninsa da Netanyahu bayan wata tattaunawar waya da suka yi kan ayyukan sojin Isra’ila a yankin.
Trump: Da Ba Don Ni Ba, Da Isra’ila Ba Ta Doron Ƙasa a Yanzu

