Gwamnan Kebbi Ya Sha Alwashin Murkushe ’Yan Bindiga



Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris, ya sha alwashin cewa gwamnati da al’ummar jihar ba za su mika wuya ga hare-haren ’yan bindiga ba, yana mai cewa za a ƙara ƙaimi wajen magance matsalar tsaro a jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a wani taron gaggawa na tsaro da ya kira a Fadar Gwamnati da ke Birnin Kebbi domin duba hanyoyin ƙarfafa tsarin tsaro da magance sabbin barazanar da ke tasowa.

Idris ya nuna damuwa kan hare-haren da suka faru a wasu sassan jihar, tare da jaddada aniyar gwamnatinsa ta tabbatar da tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ya kuma yi gargadin cewa duk wanda aka samu da laifin bai wa ’yan bindiga bayanai ko taimaka musu ta kowace hanya zai fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.

Gwamnan ya yaba wa jami’an tsaro kan ƙoƙarin da suke yi wajen tabbatar da zaman lafiya, sannan ya bukaci mazauna jihar su ci gaba da ba hukumomin tsaro sahihan bayanai domin taimakawa yaƙi da miyagun laifuka.

More from this stream

Recomended