Shugabar Makaranta Da Aka Sace A Oyo Ta Yi Kiran Gaggawa Daga Hannun Masu Garkuwa Da Su



Shugabar makaranta da aka sace a Jihar Oyo, Misis Alamu, ta roƙi gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki su gaggauta ɗaukar matakan da za su kai ga kuɓutar da ita da sauran waɗanda aka yi garkuwa da su.

A cikin wani bidiyo da ya bazu a kafafen sada zumunta, Misis Alamu ta bayyana cewa malamai da ɗaliban da ke tsare suna fuskantar mawuyacin hali sakamakon yanayin sanyi da zafin rana.

Ta kuma yi zargin cewa masu garkuwar sun fara nuna rashin haƙuri, inda ta ce sun yi barazanar cutar da ɗaya daga cikin waɗanda suke tsare da su bayan wani yunƙurin ceto da aka yi a baya.

Misis Alamu ta yi kira ga Kungiyar Malaman Najeriya (NUT), Shugaba Bola Tinubu da sauran ‘yan Najeriya da su taimaka wajen ganin an kuɓutar da su cikin gaggawa.

An dai sace ɗalibai da malamai daga al’ummomin Ahoro-Esinele da Yawota da ke ƙaramar hukumar Oriire ta Jihar Oyo a ranar 15 ga Mayu, 2026. Rahotanni sun kuma nuna cewa wani malami mai suna Michael Oyedokun, wanda ke cikin waɗanda aka sace, ya rasa ransa a hannun masu garkuwa da mutanen.

More from this stream

Recomended