Gwamnan Kwara ya shawarci Tinubu ya mayar da mafi ƙarancin albashi ₦100,000

Abdulrahaman Abdulrazak gwamnan jihar Kwara ya yi kira ga shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu da ya duba yiyuwar ƙara mafi ƙarancin albashi ya zuwa naira dubu 100.

Abdulrazak ya bayyana haka ne a ranar Juma’a a yayin wata ganawa  tsakanin Tinubu da gwamnoni a gidan shugaban ƙasar dake Lagos.

Gwamnan na jihar Kwara wanda shi ne shugaban Kungiyar Gwamnonin Najeriya ya yabawa Tinubu saboda yadda ya nuna karfin hali wajen cire tallafin man fetur.

Ya kara da cewa kaso ɗaya cikin ɗari ne kawai na yan siyasar Najeriya za su iya yin abinda shugaban ƙasar ya yi.

Ya cigaba da cewa sun yi tsammanin cewa za a samu zanga-zanga da tashin hankali bayan cire tallafin man amma kuma sai suka ga akasin haka.

Ya ce a yanzu da yawan jihohi suna biyan naira dubu ₦100 a matsayin mafi ƙarancin albashi.

“Ina shawartar shugaban ƙasa ya kamata mu zauna a tattauna kan ƙara mafi ƙarancin albashi ya zuwa 100,000,” ya ce.

More from this stream

Recomended