Tsohon Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Ya Fice Daga APC



Tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawan Najeriya, Sanata Ovie Omo-Agege, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar APC mai mulki.

A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Areh, ya fitar, Omo-Agege ya ce ya ɗauki matakin ne bayan tattaunawa da magoya bayansa da kuma la’akari da abubuwan da suka faru a APC reshen jihar Delta.

Sanatan ya ce yana ganin zai fi samun damar cimma muradunsa na siyasa da kuma yi wa al’ummarsa aiki a wata jam’iyya dabam.

Ya kuma gode wa APC bisa damar da ta ba shi na riƙe muƙamin mataimakin shugaban majalisar dattawa a majalisa ta tara, tare da yi wa jam’iyyar fatan alheri.

More from this stream

Recomended