Gwamnatin Najeriya Ta Bayar Da Hutu Domin Babbar Sallah




Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana ranakun Laraba, 27 ga watan Mayu da Alhamis, 28 ga watan Mayu a matsayin ranakun hutu domin bukukuwan Babbar Sallah a faɗin ƙasar.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren dindindin na ma’aikatar cikin gida ya fitar a madadin Ministan Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo.

Sanarwar ta bayyana cewa an ɗauki matakin ne domin bai wa Musulmin Najeriya damar gudanar da bukukuwan Sallah cikin kwanciyar hankali, tare da nuna girmamawa ga miliyoyin Musulmai a ƙasar.

Ministan ya kuma taya Musulmai murna, inda ya shawarce su da su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’o’in zaman lafiya da ci gaban Najeriya.

Idin Babbar Sallah dai na zuwa ne bayan kammala tsayuwar Arfa da mahajjata ke yi a ƙasar Saudiyya a ranar Talata.

More from this stream

Recomended