Rundunar Sojin Najeriya ta gargaɗi mazauna yankin Arewa maso Gabashin ƙasar kan yiwuwar hare-haren kunar bakin wake da na bama-bamai daga mayaƙan Boko Haram da ISWAP yayin bukukuwan Babbar Sallah.
A cikin wata sanarwa daga hedikwatar rundunar, ta bayyana cewa sahihan bayanan sirri sun nuna yiwuwar ƙungiyoyin biyu su yi amfani da lokacin bukukuwan wajen kai hare-hare kan fararen hula, musamman a wuraren da jama’a ke taruwa.
Rundunar ta ce ta tura dakarunta zuwa muhimman wurare masu haɗari, tare da ƙara amfani da na’urorin tattara bayanan sirri domin sa ido kan duk wata barazana.
Haka kuma, an ƙara yawan sintiri tare da haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro, JTF da ƙungiyoyin sa-kai domin tabbatar da tsaro a lokacin bukukuwan.
Rundunar ta shawarci jama’a da su rage zirga-zirga marasa buƙata, su guji cunkoson wurare, tare da gudanar da sallar Idi kusa da gidajensu idan ya yiwu.
Ta kuma buƙaci jama’a su rika kai rahoton duk wani abin zargi ko abubuwan da aka bari babu kulawa ga hukumomin tsaro cikin gaggawa.
Sojojin sun tabbatar da cewa suna cikin shirin ko-ta-kwana domin hana duk wani yunkuri na kawo hari a lokacin bukukuwan Sallah.
Sojojin Najeriya Sun Gargaɗi Kan Yiwuwar Hare-hare A Lokacin Babbar Sallah

