
Ko sa’o’i 48 ba ayi ba da kashe wasu mutane uku a lokacin da suke ibada tare da ɗauke wasu 15 a karamar hukumar Ekiti ta jihar Kwara sai gashi wasu yan bindigar sun yi garkuwa da mutane 10 daga fadar Sarkin Yashikira dake ƙaramar hukumar Baruten ta jihar.
A wata sanarwa da aka fitar, Adetoun Ejire-Adeyemi mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Kwara ya ce yan bindigar sun kai farmaki fadar sarkin da kuma ofishin ƴan sanda na Yashikira a lokaci guda da wajejen karfe 2:00 na daren ranar Litinin.
Sanarwar ta ce a lokacin harin ƴan bindigar sun kona wani sashe na fadar bayan sun yi garkuwa da mutane amma kuma sun fuskanci turjiya daga jami’an tsaro a lokacin da suka kai farmaki ofishin ƴan sandan inda yan sandan dake bakin aiki su ka fatattake su.
Rundunar ta ce tuni kwamishinan yan sandan jihar Ojo Adekimi ya bayar da umarni tashin wata runduna da ta ƙunshi ƴan sanda, sojoji, jami’an kula da gandun daji, yan bijilante da kuma sauran masu ruwa da tsaki a harkar tsaro inda za su bincike dazukan dake kusa domin ganin sun kuɓutar da mutanen
Kwamishinan ya yi gargadin cewa rundunar yan sandan baza ta miƙa wuya ba ga barazana ko kuma wata tsoratarwa daga wasu bata gari dake gudanar da munanan ayyukansu a jihar.

