Fitacciyar jarumar fina-finan Hausa ta Kannywood, Wasila Isma’il, ta rasu a jihar Kaduna bayan fama da rashin lafiya.
Makusantan marigayiyar sun tabbatar da cewa ta rasu ne da safiyar ranar Lahadi.
Wasila Isma’il ta rasu tana da kimanin shekaru arba’in da shida, inda ta bar ƴaƴa huɗu, mata uku da namiji ɗaya.
Marigayiyar na daga cikin tsoffin jaruman masana’antar Kannywood. Ta samu karɓuwa sosai bayan fitowarta a fim ɗin Wasila, wanda ya yi matuƙar shahara fiye da shekaru goma da suka gabata.
Rahotanni sun nuna cewa ta fara harkar fim tun a shekarar dubu ɗaya da ɗari tara da casa’in da takwas.
Baya ga harkar fim, marigayiyar ta yi aiki da gidan rediyon Liberty da ke Kaduna.
Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Isma’il Ta Rasu

