Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya lashe zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa na jam’iyyar APC da ƙuri’u miliyan goma da dubu ɗari tara da casa’in da tara da ɗari ɗaya da sittin da biyu.
Shugaban kwamitin zaɓen shugaban ƙasa na APC, Sanata Anyim Pius Anyim ne ya sanar da sakamakon bayan kammala tattara ƙuri’un da aka kaɗa a zaɓen da aka gudanar ranar Asabar a faɗin ƙasar.
Tinubu ya fafata ne da Stanley Osifo, wanda ya samu ƙuri’u dubu goma sha shida da ɗari biyar da uku kacal.
Bayan sanar da sakamakon, jam’iyyar APC ta miƙa wa Tinubu takardar shaidar lashe zaɓen tare da tutar jam’iyyar a matsayin ɗan takararta na zaɓen shugaban ƙasa na shekarar dubu biyu da ashirin da bakwai.
Daga bisani, Osifo ya taya Tinubu murnar nasarar da ya samu, inda ya gaisa da shugaban a wajen taron.
Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Ƙuri’u Sama Da Miliyan Goma

