Trump: Za Mu Ci Gaba Da Datse Tasoshin Iran Har Sai An Kammala Yarjejeniya



Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ƙasarsa za ta ci gaba da datse tasoshin ruwan Iran har sai an kammala yarjejeniyar kawo ƙarshen rikicin da ke tsakanin ƙasashen biyu.

Trump ya bayyana hakan ne yayin da ake ci gaba da tattaunawa kan matakin ƙarshe na yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin Amurka da Iran.

Tun da farko shugaban ya ce an cimma matsaya kan kawo ƙarshen yaƙin, sai dai ana ci gaba da tattauna cikakkun sharuddan yarjejeniyar.

“Za mu ci gaba da rufe tasoshin ruwansu har sai an kammala cimma matsaya, kowane ɓangare ya amince aka kuma sanya hannu,” in ji Trump.

Ya kuma jaddada muhimmancin dangantakar Amurka da Iran, amma ya ce ƙasarsa ba za ta amince Iran ta mallaki makamin nukiliya ba.

“Ba za mu yi kuskure ba, dangantakarmu da Iran za ta ci gaba da zama mai muhimmanci. Kuma ina so su fahimci cewa ba za su taɓa ƙera makamin nukiliya ba,” in ji shi.

More from this stream

Recomended