Majalisar Dinkin Duniya (UN) ta yi gargadi cewa kimanin ‘yan Najeriya miliyan talatin da biyar na fuskantar matsananciyar yunwa tsakanin watan Yuni zuwa Agusta na wannan shekara.
Hukumar jin kai ta UN ta bayyana hakan a cikin wani rahoto, inda ta ce Najeriya na fuskantar matsalar karancin abinci mai tsanani, musamman yayin lokacin rani da ake kira “lean season”.
Rahoton ya nuna cewa kusan mutum ɗaya cikin bakwai a Najeriya zai iya fuskantar rashin isasshen abinci, lamarin da ya fi kamari a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas.
UN ta kuma ce kimanin yara miliyan shida da dubu ɗari huɗu na iya fama da matsananciyar tamowa a waɗannan yankuna a bana.
Hukumar ta yi kira da a gaggauta tallafin jin kai domin rage illar matsalar, tana mai gargadin cewa jinkirin taimako zai tilasta iyalai rage yawan abinci, sayar da kadarori ko kuma fitar da yara daga makaranta.
Rahoton ya kuma nuna cewa daga cikin dala miliyan dari biyar da sha shida da ake bukata domin shirin jin kai na shekarar 2026, an samu kusan kashi arba’in kacal na kudin da ake bukata zuwa yanzu.
MDD: Mutane Miliyan Talatin Da Biyar A Najeriya Na Fuskantar Matsananciyar Yunwa

