Ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta bayyana cewa gobara ta tashi a wani ɓangare na cibiyar nukiliyar ƙasar da ke yankin Al Dhafra bayan harin jirgin mara matuƙi.
Rahotanni sun ce harin ya afka wa wani injin wuta da ke wajen tashar nukiliyar Barakah.
Hukumomin ƙasar sun tabbatar da cewa babu wanda ya jikkata ko ya rasa rai sakamakon lamarin.
Sun kuma ce harin bai haifar da wata illa ga tashar nukiliyar ba, yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da bincike kan abin da ya faru.
Gobara Ta Tashi A Wajen Cibiyar Nukiliyar UAE Bayan Harin Jirgin Mara Matuƙi

