Kungiyar Fulani Ta Zargi ‘Yan Bindigar Berom Da Kai Musu Hare-Hare A Filato



Kungiyar Gan Allah Fulani Development Association (GAFDAN) ta sake zargin wasu kungiyoyin matasa da ta kira ‘yan bindigar Berom da kai hare-hare kan makiyaya Fulani tare da kashe shanunsu a wasu yankuna na Jihar Filato.

A wata sanarwa da kungiyar ta fitar a ranar Talata, ta ce an samu hare-hare da dama a kan makiyaya a kananan hukumomin Barkin Ladi da Riyom da kuma Jos ta Gabas. Ta kuma koka cewa duk da kai rahotannin wadannan hare-hare ga jami’an tsaro, ba a dauki matakin da ya dace ba.

Kungiyar ta ambaci wani hari da aka kai a Riyom, inda ta ce an tare wani makiyayi mai suna Usaini Abubakar, tare da harbe shanunsa guda shida.

A cewar kungiyar, lamarin ya faru ne yayin da shanun ke kiwo cikin lumana ba tare da wata tsokana ba, inda ta bayyana hakan a matsayin abin damuwa da ke barazana ga zaman lafiya a yankin.

Har ila yau, GAFDAN ta yi zargin cewa wasu matasan Berom sun kai hari kan wasu matasa Fulani biyu a kauyen Gada da ke Jos ta Gabas, inda aka doke su tare da lalata babura nasu.

Kungiyar ta ce duk da kai rahoton lamarin ga jami’an tsaro, babu wanda aka kama.

A karshe, kungiyar ta bukaci hukumomin tsaro su gudanar da bincike mai zurfi kan hare-haren tare da kamo wadanda ake zargi domin gurfanar da su a gaban kuliya. Ta kuma bukaci daukar matakan kare makiyaya da dukiyoyinsu, tare da kira ga al’ummomi da su rungumi zaman lafiya da tattaunawa domin kauce wa rikici.

More from this stream

Recomended