Isra’ila Za Ta Ƙara Tura Sojoji Zuwa Lebanon

Ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya ce an umarci rundunar sojin ƙasar, IDF, da ta yi amfani da dukkan ƙarfinta a Lebanon idan aka sake kai hari kan sojojinta.

Wannan na zuwa ne bayan kashe wani sojan Isra’ila a ranar Asabar a Lebanon, duk da cewa an fara aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta.

Katz ya bayyana cewa, duk da yarjejeniyar, Isra’ila za ta ƙara tura sojojin ƙasa da na sama zuwa ƙasar domin ƙarfafa tsaro.

Rahotanni sun nuna cewa yarjejeniyar tsagaita wutar na fuskantar barazana bayan kisan sojan Isra’ila da kuma wani jami’in kiyaye zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya daga Faransa.

Ana sa ran a ranar Talata Shugaban Faransa, Emmanuel Macron, zai gana da Firaministan Lebanon, Nawaf Salam, a birnin Paris domin tattauna batun tsagaita wutar.

More from this stream

Recomended