Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Mohammed Hayatu-Deen, ya fice daga jam’iyyar tare da komawa African Democratic Congress (ADC), inda ya ce dalilinsa shi ne matsalar tsaro da ke ƙara ta’azzara, hauhawar farashin rayuwa, da kuma damuwa kan raguwar sararin dimokuraɗiyya a Najeriya.
Hayatu-Deen ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, inda ya ce ya yanke shawarar shiga ADC ne domin neman wata sahihiyar madadin siyasa da za ta iya magance matsalolin tsaro, daidaita tattalin arziki, da samar da ayyukan yi gabanin zaɓen 2027.
A cewarsa, rikicin cikin gida da PDP ke fama da shi a matakin ƙasa ya sa wasu manyan ‘yan jam’iyyar ke ficewa zuwa APC mai mulki ko kuma ADC.
Ya ce zai yi amfani da gogewarsa a harkokin kasuwanci da gyaran tattalin arziki wajen tallafa wa jam’iyyar ADC, tare da cewa zai yi kamfen sosai domin ganin jam’iyyar ta yi nasara a zaɓen 2027.
Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a PDP ya fice daga jam’iyyar don komawa ADC

