An kashe mutane 11 tare da kona gidaje 50 a rikicin kabilanci a jihar Nasarawa

Wasu mutane da ake zargin batagari ne sun kashe aƙalla mutane 11 tare da kone gidaje sama da 50 a garuruwan Akyawa da Udege dake karamar hukumar Nasarawa ta jihar Nasarawa.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Nasarawa Ramhan Nansel  ya bayyana cewa harin da aka kai ranar Juma’a  na ramuwa gayya ne  kan kisan mutane biyu da suka fito daga ƙabilar maharan.

Nansel ya kara da cewa kwamishinan yan sandan jihar, Shetima  Mohammed ya ziyarci yankin da abun ya faru inda ya nuna matuƙar damuwarsa kan mummunan lamarin.

“Ya jajantawa iyalan waɗanda abin ya shafa da kuma al’ummar gari baki ɗaya inda ya tabbatar musu cewa rundunar ta ci alwashin tabbatar da anyi adalci ta hanyar hukunci,” ya ce

Ya kara da cewa kwamishina Shettima ya bayar da umarnin fara farautar waɗanda su ka kai harin domin kama su tare da gurfanar da su a gaban shari’a.

A yayin zaman  tattaunawa tare da masu ruwa da tsaki kwamishinan ya shawarci al’ummar da su kwantar da hankalinsu tare da bin doka da oda kana su taimakawa jami’an tsaro da bayanai da za su taimaka wajen kama waɗanda su ka aikata laifin.

More from this stream

Recomended