ICPC ta shirya gurfanar da El-Rufai a gaban kotu a Kaduna

Hukumar ICPC dake hana ci da karɓar rashawa ta  sanar da cewa a ranar Tal za ta gurfanar da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai a gaban kotu.

El-Rufai ya shafe kwanaki a tsare tun bayan da ya kai kansa ofishin hukumar EFCC a ranar 16 ga watan Fabrairu bayan da ya amsa gayyatar da hukumar ta yi masa.

Tsohon gwamnan ya shafe kwanaki biyu yana amsa tambayoyi a hannun EFCC kafin jami’an hukumar ICPC su ɗora daga inda jami’an EFCC suka tsaya.

A wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin, John Okafor mai magana da yawun hukumar ta ICPC ya ce za a gurfanar da El-Rufai a gaban Babbar Kotun Tarayya dake Kaduna a ranar Talata ne.

Tsawon lokacin da aka ɗauka ba tare da an gurfanar da El-Rufai a gaban kotu ba ya jawo cece-kuce inda ƙungiyoyi da dama da kuma dai-daikun mutane suka riƙa kiraye-kirayen a sake shi ko kuma a gurfanar da shi a gaban kotu.

More from this stream

Recomended