Rundunar juyin-juya halin Iran ta sanar da cewa ta harbo wani jirgin yaƙin Isra’ila mai suna F-16 a sararin samaniyarta.
Kamfanin dillancin labarai na ƙasar, IRNA, ya rawaito wata sanarwa daga rundunar inda ta ce an harbo jirgin ne da asubahin yau a tsakiyar ƙasar.
Sanarwar ta ƙara da cewa wannan shi ne jirgin Isra’ila na uku da suka harbo tun bayan fara rikicin, sai dai ba a bayar da cikakken bayani kan sauran biyun ba. Haka kuma, rundunar ba ta fayyace inda jirgin ya faɗi ba bayan an harbe shi.
Sai dai rundunar sojin Isra’ila ta ce ɗaya daga cikin jiragen yaƙinta ya fuskanci harin makami mai linzami da aka harba daga ƙasa, amma harin bai yi nasara ba.
A cikin sanarwar da ta fitar, rundunar ta ce, “a lokacin ayyukan rundunar sojin saman Isra’ila, wani makami mai linzami da ka harba daga ƙasa ya yi yunƙurin harbo ɗaya daga jirgin jiragen yaƙinta. To amma harin bai samu nasara ba, kuma babu lahanin da aka yi wa jirgin, sannan aikinmu bai samu tangarɗa ba.”
Lamarin ya ƙara nuna yadda ɓangarorin biyu ke ci gaba da bayar da rahotanni masu karo da juna dangane da halin da ake ciki.
Iran Ta Ce Ta Harbo Jirgin Yaƙin Isra’ila, Isra’ila Ta Musanta

