Tsohon shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa Amurka da Isra’ila sun samu gagarumar nasara a kan sojojin ruwa da na sama da kuma jagororin Iran.
A cewarsa, “Mun gama da komai,” sannan ya kara da cewa “nasarar ta ma wuce abin da muka tsammata”.
Lokacin da aka tambaye shi ko yana da shirin tura sojojin Amurka zuwa yankin, Trump ya bayyana cewa babu inda za a tura sojojin kasar.
Sai dai, lokacin da aka sake matsa masa da tambaya kan yiwuwar daukar irin wannan mataki, ya ce “ba zan fada maka ba”.
Trump Ya Ce Amurka Da Isra’ila Sun Yi Nasara A Kan Iran

