Majalisar dattawa ta tabbatar da Taiwo Oyedele a matsayin minista

A ranar Laraba ne majalissar dattawa ta tabbatar da Taiwo Oyedele a matsayin karamin ministan a ma’aikatar kuɗi.

Majalisar ta tabbatar da shi ne biyo bayan tantacewar da ta yi masa inda ya amsa tambayoyi a gabanta.

A makon da ya gabata ne shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya mikawa majalisar sunan Oyedele domin ta sahale masa ya naɗa shi a matsayin minista kuma mamba a majalisar zartarwa ta tarayya .

Kafin a naɗa shi muƙamin ministan Oyedele shi ne shugaban kwamitin shugaban kasa kan batun haraji.

Oyedele zai maye gurbin tsohuwar ministar ma’aikatar, Doris  Uzoka Anite.

More from this stream

Recomended