
John Tsoho, babban alkalin kotun tarayya ya naɗa sabon alkali da zai saurari kararraki biyu da hukumar EFCC ta gurfanar da tsohon babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami.
Yanzu dai an tura kararrakin gaban mai shari’a, Joyce Abdulmalik wacce ta sanya ranar 27 ga watan Fabrairu domin fara sauraren ƙarar.
An sake tura karar gaban sabon alkali ne bayan da mai shari’a Obiora Egwuatu ya sanar da janye kansa daga sauraren ƙarar.
A ranar 12 ga watan Fabrairu ne Obiora ya sanar da cewa ya janye kansa daga sauraren kararraki biyu bisa raɗin kansa.
Hukumar EFCC na tuhumar Malami da aikata laifukan guda 16 da suka shafi almundahanar kudade.

