Fadar shugaban ƙasa ta zargi Adeyemi Adeniyi Mathew da kasancewa ɗan damfara da ya naɗa kansa shugaban wata hukumar neman tallafi daga ƙasashen waje tare da buɗe ofis a ginin Sakatariyar Gwamnatin Tarayya.
Adeyemi ya yi ikirarin cewa mai bai wa shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa shawara ne ya naɗa shi a mukamin, amma shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila, ya musanta wannan zargi.
Gwamnatin tarayya ta kuma buƙaci ‘yan ƙasa da su guji yaɗa jita-jita ko yin shaci-faɗi kan lamarin, tana mai cewa batun yana gaban kotu domin ci gaba da shari’a.
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Zargi Wani Mutum Da Samar Da Wata Ma’aikatar Gwamnati Ta Bogi

