
Wata gobara da ta kama ta cinye wani sashe na babbar kasuwar Fika dake karamar hukumar Fika ta jihar Yobe inda ta kone kayayyaki da kuma kassara hada-hadar kasuwanci.
Gobarar wacce ta fara da tsakar daren ranar Litinin ta kone shaguna masu yawa da kuma rumfuna.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin babban sakataren hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Yobe, Dr Muhammad Goje ya ce jami’an kai daukin gaggawa sun isa wurin akan lokaci domin shawo kan gobarar da kuma hana ta cigaba da yin barna.
“Mun samu rahoton kiran kai daukin gaggawa na gobara da ta kama babbar kasuwar Fika a karamar hukumar Fika jami’an kai daukin gaggawar mu tare da haÉ—in gwiwar jami’an kashe gobara yanzu haka su na wurin suna aiki tukuru dan ganin sun kashe wutar da kuma dakatar da barna,” a cewar Goje
Ya ce gobarar na zuwa ne jim kaɗan bayan da hukumar ta duba rahoto tare da kammala tsarin da za abi wajen taimakawa yan kasuwar da gobara ta yiwa ɓarna a Bukarti da wasu wurare uku

