Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 6 a Benue

Da asubahin ranar Talata ne wasu yan bindiga suka yi garkuwa da wasu matafiya shida a kusa da kauyen Kula dake kan lalatacciyar hanyar Naka zuwa Makurdi a  karamar hukumar Gwer West ta jihar Benue.

A cewar jaridar Daily Trust tuni masu garkuwar suka tuntubi iyalan mutanen sa’o’i biyu bayan garkuwar inda suka buƙata biya sue naira miliyan 100 a matsayin kuɗin fansa.

Wani da ya sheda faruwar lamarin ya ce mutanen da suka hada da maza uku da mata uku na tafiya ne a cikin jerin gwanon motoci lokacin da aka tsare su tare da yin awon gaba da su.

Rahotanni sun bayyana cewa hudu daga cikin mutanen da aka yi garkuwar da su mambobine na ƙungiyar addinin musulunci ta Ansaruddeen wanda su ka  tawo daga birnin Ilorin na jihar Kwara a ranar Litinin inda suka iso Naka da tsakar dare.

Mijin ɗaya daga cikin matan da abun ya rutsa da su ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce masu garkuwar sun tuntube su kusan sa’o’i biyu bayan faruwar lamarin kuma sun bukaci a biya su miliyan 100 a matsayin kuɗin fansa.

Victor Ormin shugaban ƙaramar hukumar Gwer West ya tabbatarwa da yan jaridu faruwar lamarin lokacin da ya ke zantawa da su a Makurdi.

More from this stream

Recomended