Gwamnatin tarayya ta bawa yan kasuwar Singa tallafin biliyan ₦5

Gwamnatin tarayya ta sanar da bayar da tallafin naira biliyan 5 ga mutanen da bala’in gobarar kasuwar Singa ya shafa.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima  ne ya sanar da haka a ranar Litinin a yayin ziyarar jaje da ya kai kasuwar inda gobara ta kone dukiya ta biliyoyin naira.

Shettima ya bayyana gobarar a matsayin wata masifa da ta shafi kasa baki daya ya ce asarar da aka yi ba Kano kaɗai ta shafa ba fa ce kasa baki ɗaya.

Ya yi addu’a ga mutanen da abun ya shafa da kuma rokon Allah ya kare faruwar haka anan gaba.

A yayin ziyarar mataimakin shugaban kasar na tare da gwamnonin jihohin Imo, Jigawa da kuma Kebbi.

Shugaban kungiyar kasuwar Singa, Alhaji Junaidu Muhammad ya yabawa gwamnatin tarayya kan tallafin da ta kawo a lokacin da ya da ce.

Ya tabbatar da cewa za ayi amfani da kuɗin yadda ya kamata wajen tallafawa yan kasuwar da abun ya shafa.

More from this stream

Recomended