Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta yi Allah wadai da kisan kimanin mutane 170 da aka yi a Jihar Kwara, inda ta ce harin ya nuna gazawar tsaro a karkashin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na ƙasa na jam’iyyar, Mallam Bolaji Abdullahi, ya sanya wa hannu, ADC ta ce kisan gillar da aka yi a ƙaramar hukumar Kaiama alama ce da ke nuna cewa matakan da gwamnati ke ɗauka kan matsalar tsaro ba sa aiki yadda ya kamata.
Jam’iyyar ta kuma tambayi makomar ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro da shugaban ƙasa ya sanar a watan Nuwamban 2025, tare da alkawarin ɗaukar dubban sabbin ‘yan sanda aiki. Ta ce yawaitar kashe-kashen jama’a na nuni da cewa ko dai matakan ba su yi tasiri ba ko kuma ba a aiwatar da su yadda ya kamata ba.
Jam’iyyar ta kuma nuna damuwa cewa yawan motsin jami’an tsaro da aka gani bara na iya zama na ganin ido ne kawai, ba wai domin kare rayukan ‘yan ƙasa ba.
ADC Ta Dora Alhakin Kisan Kwara Kan Gwamnatin Tinubu

