Atiku, El-Rufai da sauransu sun nemi a yi musu rijistar sabuwar jam’iya

Jagororin yan adawa a karkashin inuwar Nigeria National Coalition Group (NNCG) sun fito da zabi All Democratic Alliance(ADA) a matsayin jam’iyar da za  su kafa domin kalubalantar jam’iyar APC a zaben shekarar 2027.

NNCG ta mika bukata a hukumance wurin hukumar zabe mai zaman kanta ta  kasa INEC domin ta yi mata rijista a matsayin jam’iyar siyasa gabanin zaben kasa baki daya Mai zuwa.

An aikewa da shugaban hukumar INEC, Mahmud  Yakubu takardar neman a yiwa gamayyar rijistar jam’iyar siyasa mai dauke da kwanan watan 19 ga watan Yuni inda take dauke da sahannun shugabanta Chief Akin Ricketts da kuma sakataren wucin gadi Abdullahi Musa Elayo.

Wasikar wacce ke dauke da sitamfi na shedar karbar hukumar INEC na ranar 20 ga watan Yuni an yi mata lakabin “Bukatar neman yin rijista a matsayin jam’iyar siyasa,” mai suna ADA da kuma alama.

Tun da farko mambobin gamayyar hadakan sun nemi shiga cikin jam’iyun da ake da su amma daga bisani suka yanke shawarar kafa sabuwar jam’iya.

More from this stream

Recomended