
Kungiyar Sanatocin Arewa(NSF) ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta samarwa da sojoji da kuma sauran jami’an tsaro makamai na zamani domin su yi yaki ta’addanci da kuma fadace-fadace a fadin kasa baki daya.
A wata sanarwa da aka fitar ranar Laraba dake dauke da sahannun shugaban kungiyar, Sanata Abdulaziz Musa, sanatocin sun yi allawadai da harin baya-bayannan da aka kai jihar Benue inda aka kashe mutane sama da 100.
Yan majalisar dattawan sun kuma mika sakon ta’aziya ga iyalan wadanda suka jikkata tare da fatan samun sauki ga wadanda suka jikkata a harin.
Sanatocin sun yabawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kan ziyarar da ya kai jihar Benue sun kuma shawarci gwamnatin tarayya da ta dauki kwararan matakai na ganin cewa anyi adalci tare da kare faruwar haka anan gaba.