Tinubu na kewa aiki ba APC – Wike

Tsohon gwamnan jihar Rivers kuma ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce shi yana aiki da shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ne ba jam’iya ba.

Da yake magana yayin wata tattaunawa da gidan talabijin na Channels a ranar Laraba Wike ya ce shi ba ɗan jam’iyar APC ba ne kuma ba jam’iyar yake wa aiki ba.

Naɗin muƙamin minista da aka yiwa Wike a gwamnatin Tinubu ta jam’iyar ya sa mutane sun bayyana ra’ayi ma bambanta da dama.

Da aka tambaye shi a yayin ganawar kan kasancewarsa mamba a jam’iyar PDP, tsohon gwamnan ya ce har yanzu yana nan a cikin jam’iyar PDP.

Ya ce ya karbi mukamin ne domin ya taimakawa shugaban kasa ba wai jam’iya ba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]